1 Corinthians 4

1Ga yadda za ku dauke mu, kamar bayin Almasihu da kuma masu rikon asiran Allah. 2Hade da wannan, ana bukatar wakilai su zama amintattu.

3Amma a gare ni, karamin abu ne ku yi mani shari’a, ko a wata kotu irin ta mutane. Gama bani yi wa kaina shari’a. 4Ban sani ko akwai wani zargi a kaina ba, amma wannan bai nuna cewa bani da laifi ba. Ubangiji ne mai yi mani shari’a.

5Sabili da haka, kada ku yanke shari’a kafin lokaci, kafin Ubangiji ya dawo. Zai bayyana dukkan boyayyun ayyuka na duhu, ya kuma tona nufe-nufen zuciya. San nan kowa zai samu yabonsa daga wurin Allah.

6Yan’uwa, ina dora wadannan ka’idoji a kaina da Afollos domin ku, yadda ta wurin mu za ku koyi ma’anar maganar nan cewa, “kada ku zarce abin da aka rubuta.” Ya zama haka domin kada waninku ya kumbura yana nuna fifiko ga wani akan wani. 7Gama wa yaga bambanci tsakanin ku da wasu? Me kuke da shi da ba kyauta kuka karba ba? Idan kyauta kuka karba, don me kuke fahariya kamar ba haka ba ne?

8Kun rigaya kun sami dukkan abubuwan da kuke bukata! Kun rigaya kun zama mawadata! Kun rigaya kun fara mulki- kuma ba tare da mu ba! Hakika, marmarina shine ku yi mulki, domin mu yi mulki tare da ku. 9A tunanina, mu manzanni, Allah ya sa mu a jerin karshe kamar mutanen da aka zartar wa hukuncin mutuwa. Mun zama abin kallo ga duniya, ga mala’iku, ga mutane kuma.

10Mun zama marasa wayo sabili da Almasihu, amma ku masu hikima ne a cikin Almasihu. Mu raunana ne, amma ku masu karfi ne. Ana ganin mu marasa daraja, ku kuwa masu daraja. 11Har zuwa wannan sa’a, muna masu yunwa da kishi, marasa tufafi masu kyau, mun sha kazamin duka, kuma mun zama marasa gidaje.

12Mun yi fama sosai, muna aiki da hanuwanmu. Sa’adda an aibata mu, muna sa albarka. Sa’adda an tsananta mana, muna jurewa. 13Sa’adda an zage mu, muna magana da nasiha. Mun zama, kuma har yanzu an dauke mu a matsayin kayan shara na duniya da abubuwa mafi kazamta duka.

14Ban rubuta wadannan abubuwa domin in kunyata ku ba, amma domin in yi maku gyara kamar kaunatattun yayana. 15Ko da kuna da masu riko dubu goma a cikin Almasihu, ba ku da ubanni da yawa. Gama ni na zama ubanku cikin Almasihu Yesu ta wurin bishara. 16Don haka, ina kira gare ku da ku zama masu koyi da ni.

17Shiyasa na aiko Timoti wurin ku, kaunatacce da amintaccen dana cikin Ubangiji. Zai tunashe ku hanyoyina cikin Almasihu, kamar yadda nake koyar da su ko’ina da kowace Ikilisiya. 18Amma yanzu, wadansun ku sun zama masu fahariya, suna yin kamar ba zan zo wurinku ba.

19Amma zan zo gare ku ba da dadewa ba, idan Ubangiji ya nufa. Sannan zan san fiye da maganar masu fahariya, amma kuma zan ga ikonsu. 20Gama Mulkin Allah ba magana kadai ya kunsa ba, amma ya kunshi iko. Me kuke so? In zo wurin ku da sanda ne ko kuwa da kauna da ruhun nasiha?

21

Copyright information for HauULB